17/06/2026
Gwamna Radda Ya Gargaɗi ’Yan Social Media Kan Yaɗa Bidiyon Mutanen da Aka Yi Garkuwa da Su
Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira ga masu tasiri a kafafen sada zumunta, masu rubutun yanar gizo (bloggers) da masu ƙirƙirar abun ciki na intanet da su riƙa nuna ƙwarewa da ɗa’a wajen yaɗa labaran da s**a shafi matsalolin tsaro.
Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan wata ganawa da ya yi da malamai da sauran masu ruwa da tsaki a Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, inda ya kuma sanar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ɗaukar jami’an Katsina Forest Guards 1,000 domin ƙarfafa tsaro a jihar.
Radda ya yi gargaɗi kan yaɗa bidiyoyin mutanen da aka yi garkuwa da su, yana mai cewa irin waɗannan bidiyoyi na ƙara wa iyalan waɗanda abin ya shafa radadi da damuwa, tare da iya kawo cikas ga ayyukan jami’an tsaro.
Ya ce abin takaici ne yadda wasu ke yaɗa bidiyon waɗanda aka sace, har ma idan danginsu ne ko iyayensu, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da bai dace ba kuma ba ya taimakawa ƙoƙarin dawo da zaman lafiya.
“Ina kira ga masu tasiri a kafafen sada zumunta da bloggers da su taka rawar gani wajen magance matsalar tsaro. Wasu na amfani da dandalinsu wajen yaɗa bidiyoyi masu tayar da hankali na waɗanda aka yi garkuwa da su yayin da suke hannun masu garkuwa, kuma hakan ba ya taimakawa ƙoƙarin da ake yi,” in ji Gwamna Radda.
Gwamnan ya jaddada cewa sahihin rahoto da bin ƙa’idojin aikin jarida na da muhimmanci wajen tallafa wa jami’an tsaro, kare martabar waɗanda abin ya shafa da kuma rage raɗaɗin da iyalansu ke fuskanta.