Voice of katsina

Voice of katsina VoiceofKatsina a dynamic media forum
Truth, Transparency, advocacy & progress(T-TAP)

Make it easy for you...

Gwamna Radda Ya Gargaɗi ’Yan Social Media Kan Yaɗa Bidiyon Mutanen da Aka Yi Garkuwa da SuGwamnan Jihar Katsina, Malam D...
17/06/2026

Gwamna Radda Ya Gargaɗi ’Yan Social Media Kan Yaɗa Bidiyon Mutanen da Aka Yi Garkuwa da Su

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya yi kira ga masu tasiri a kafafen sada zumunta, masu rubutun yanar gizo (bloggers) da masu ƙirƙirar abun ciki na intanet da su riƙa nuna ƙwarewa da ɗa’a wajen yaɗa labaran da s**a shafi matsalolin tsaro.

Gwamnan ya bayyana hakan ne bayan wata ganawa da ya yi da malamai da sauran masu ruwa da tsaki a Fadar Gwamnatin Jihar Katsina, inda ya kuma sanar da cewa Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ɗaukar jami’an Katsina Forest Guards 1,000 domin ƙarfafa tsaro a jihar.

Radda ya yi gargaɗi kan yaɗa bidiyoyin mutanen da aka yi garkuwa da su, yana mai cewa irin waɗannan bidiyoyi na ƙara wa iyalan waɗanda abin ya shafa radadi da damuwa, tare da iya kawo cikas ga ayyukan jami’an tsaro.

Ya ce abin takaici ne yadda wasu ke yaɗa bidiyon waɗanda aka sace, har ma idan danginsu ne ko iyayensu, yana mai bayyana hakan a matsayin abin da bai dace ba kuma ba ya taimakawa ƙoƙarin dawo da zaman lafiya.

“Ina kira ga masu tasiri a kafafen sada zumunta da bloggers da su taka rawar gani wajen magance matsalar tsaro. Wasu na amfani da dandalinsu wajen yaɗa bidiyoyi masu tayar da hankali na waɗanda aka yi garkuwa da su yayin da suke hannun masu garkuwa, kuma hakan ba ya taimakawa ƙoƙarin da ake yi,” in ji Gwamna Radda.

Gwamnan ya jaddada cewa sahihin rahoto da bin ƙa’idojin aikin jarida na da muhimmanci wajen tallafa wa jami’an tsaro, kare martabar waɗanda abin ya shafa da kuma rage raɗaɗin da iyalansu ke fuskanta.

Tinubu Ya Amince da Ɗaukar Jami’an Katsina Forest Guard 1,000 Domin Ƙarfafa Yaƙi da ’Yan BindigaGwamnan Jihar Katsina, M...
16/06/2026

Tinubu Ya Amince da Ɗaukar Jami’an Katsina Forest Guard 1,000 Domin Ƙarfafa Yaƙi da ’Yan Bindiga

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya bayyana cewa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya amince da ɗaukar sabbin jami’an tsaron dazuka (Katsina Forest Guards) guda 1,000 domin ƙara ƙarfafa yaƙi da matsalar tsaro a jihar.

Gwamnan ya ce shugaban ƙasar ya ba gwamnatin jihar izinin ɗaukar jami’an ne domin su rika kula da tsaron dazukan jihar da kuma taimakawa hukumomin tsaro wajen daƙile ayyukan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

“Shugaban Ƙasa Tinubu ya ba mu umarnin ɗaukar jami’an tsaro 1,000 da za su kula da tsaron dazukan Jihar Katsina domin inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” in ji Gwamna Radda.

Matakin na zuwa ne yayin da gwamnatin jihar ke ci gaba da aiwatar da sabbin dabarun yaƙi da rashin tsaro, ciki har da ƙarfafa haɗin gwiwa da jami’an tsaro da kuma samar da kayan aiki da tallafin da s**a dace.

Masu lura da al’amuran tsaro na ganin cewa ƙara yawan jami’an da za su rika sintiri a dazuka na iya taimakawa wajen rage hare-haren ’yan bindiga da kuma hana su samun mafaka a yankunan dazukan jihar.

Gwamnatin Katsina Ta Haramta Babura, POS da Wuraren Cajin Waya a Matazu da Musawa; Mataki Irin Wanda Aka Taɓa Ɗauka a Za...
16/06/2026

Gwamnatin Katsina Ta Haramta Babura, POS da Wuraren Cajin Waya a Matazu da Musawa; Mataki Irin Wanda Aka Taɓa Ɗauka a Zamanin Masari

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda, ya sanar da wasu sabbin tsauraran matakan tsaro da nufin ƙarfafa yaƙi da ayyukan ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane a jihar.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar bayan taron gaggawa na tsaro, an haramta saye, sayarwa, jigilar man fetur da adana shi a cikin jarkoki a faɗin jihar domin dakile hanyoyin da ake zargin masu laifi ke samun man fetur.

Haka kuma, gwamnatin ta ba da umarnin rufe dukkan harkokin POS da wuraren cajin waya na kasuwanci a ƙananan hukumomin Matazu da Musawa, tare da haramta amfani da babura gaba ɗaya a yankunan biyu.

Gwamnatin ta bayyana cewa matakan na daga cikin sabbin dabarun tsaro da ake ɗauka domin murƙushe ayyukan masu laifi da dawo da zaman lafiya a yankunan da matsalar tsaro ta fi kamari.

Sai dai masu lura da al’amuran tsaro sun nuna cewa wannan ba shi ne karo na farko da gwamnatin Katsina ke ɗaukar irin waɗannan matakai ba.

A lokacin gwamnatin tsohon gwamna Aminu Bello Masari, an taɓa aiwatar da makamantan matakan a ƙananan hukumomin Dutsin-Ma, Safana, Batsari da Dan Musa, inda har aka dakatar da ayyukan hanyoyin sadarwa na waya da intanet na wani lokaci domin hana ’yan bindiga amfani da su wajen sadarwa da tsara hare-hare.

A wancan lokaci, mazauna yankunan sun shafe kwanaki da makonni ba tare da damar yin kira ko amfani da intanet ba, yayin da hukumomin tsaro ke gudanar da manyan ayyukan daƙile ta’addanci.

Sabbin matakan da gwamnatin Radda ta ɗauka na ci gaba da jawo muhawara, inda wasu ke ganin wajibi ne domin dawo da tsaro, yayin da wasu ke nuna damuwa kan tasirin da za su iya yi ga harkokin yau da kullum da kasuwancin al’umma.

Gwamnatin Jihar Katsina ta ayyana ranar Talata, 16 ga watan Yuni, 2026 a matsayin ranar hutu ta musamman ga ma’aikata do...
15/06/2026

Gwamnatin Jihar Katsina ta ayyana ranar Talata, 16 ga watan Yuni, 2026 a matsayin ranar hutu ta musamman ga ma’aikata domin murnar shigowar Sabuwar Shekarar Musulunci ta 1448 bayan Hijira (1 Muharram 1448 AH).

Wannan sanarwa ta biyo bayan tabbacin da Majalisar Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammad Sa’ad Abubakar III ta yi, cewa Talata ce za ta kasance 1 ga watan Muharram, bayan kammala tantance rahotannin ganin jinjirin watan a sassa daban-daban na ƙasar nan.

A cewar sanarwar, an tabbatar da ganin watan Muharram bisa tsarin shari’ar Musulunci, wanda ke nuni da fara sabon zagayen kalandar Musulunci ta Hijira, wato shekarar 1448H.

Muharram na daga cikin watanni huɗu masu alfarma a addinin Musulunci, kuma shi ne watan farko a kalandar Hijira da Musulmai ke amfani da ita wajen lissafin shekarunsu da muhimman lokuta na addini.

A yayin da ake shiga sabuwar shekarar, malamai da shugabannin addini sun yi kira ga al’umma da su yi amfani da wannan dama wajen ƙara kusanci da Allah, da kuma yin addu’o’i na zaman lafiya, haɗin kai, da ci gaban ƙasa baki ɗaya.

Allah Ya sanya Sabuwar Shekarar 1448H ta kasance shekara mai albarka, zaman lafiya da nasara ga al’ummar Musulmi da ƙasa baki ɗaya.

Gwamnatin Kano Ta Ware Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin Auren Gata Na Mutane 3,000Gwamnatin Jihar Kano ta ware Naira biliy...
15/06/2026

Gwamnatin Kano Ta Ware Naira Biliyan 1.5 Domin Shirin Auren Gata Na Mutane 3,000

Gwamnatin Jihar Kano ta ware Naira biliyan 1.5 domin gudanar da shirin auren gata da ake shirin yi wa mutum 3,000 a faɗin jihar.

Babban Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Kano, Sheikh Ibrahim Daurawa, ne ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Litinin, inda ya ce kuɗaɗen za su rufe dukkanin buƙatun shirin.

A cewarsa, za a kashe wani ɓangare na kuɗaɗen wajen samar da kayan ɗaki, kayan abinci, sadaki, kayan sawa ga ma’auratan, da kuma jarin Naira 100,000 da za a bai wa kowace amarya domin fara rayuwar aure.

Daurawa ya kuma bayyana cewa Hukumar Hisbah tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano sun fara gudanar da gwaje-gwajen lafiya ga waɗanda za su amfana da shirin domin tabbatar da lafiyarsu kafin ɗaura aure.

Shirin auren gata na daga cikin shirye-shiryen gwamnatin jihar da ke da nufin tallafa wa matasa da marasa ƙarfi wajen samun damar yin aure da kuma gina iyalai masu ɗorewa.

Jami’an Tsaro Sun Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun ’Yan Bindiga a KatsinaRahotanni da ke shigo mana s...
15/06/2026

Jami’an Tsaro Sun Ceto Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Daga Hannun ’Yan Bindiga a Katsina

Rahotanni da ke shigo mana sun tabbatar da cewa jami’an tsaro sun yi nasarar ceto matar marigayi Manjo Janar Rabe Abubakar (Rtd.) daga hannun masu garkuwa da mutane a Jihar Katsina.

Wannan na zuwa ne bayan rasuwar tsohon babban jami’in sojin Najeriyar a lokacin da yake tsare a hannun masu garkuwa da shi, lamarin da ya jefa al’umma cikin alhini da jimami.

Duk da cewa har yanzu ana jimamin rasuwar marigayin Janar Rabe Abubakar, an samu sauƙin zuciya da farin ciki sakamakon samun ’yancin matarsa da kuma dawowarta cikin aminci.

Muna addu’ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙan marigayi Janar Rabe Abubakar, Ya gafarta masa kura-kuransa, Ya sanya shi a Aljannatul Firdausi, sannan Ya bai wa iyalansa haƙuri da juriyar wannan babban rashi.

Haka kuma muna yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu da sadaukarwar da suke yi wajen kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Allah Ya ƙara taimakon dakarunmu, Ya tabbatar da zaman lafiya a ƙasarmu. Amin.

14/06/2026

Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, Dr. Aminu Usman (Abu Ammar), ya bayyana cewa mafi yawan matasan da ake samu a wuraren da ake aikata bidala da sauran ayyukan barna a jihar sun fito ne daga iyalan talakawa.

Dr. Aminu Usman ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Mobile Media Crew, inda ya ce bincike da gogewar da hukumar ke da ita a ayyukanta na yau da kullum sun nuna cewa matsalolin tattalin arziki, rashin kulawa da tarbiyya na daga cikin abubuwan da ke jefa wasu matasa cikin miyagun ɗabi’u.

”‘Ya’yan Talakawa Ne S**a Fi Yawa a Wuraren da Ake Aikata Bidala da Barna a Katsina” — Kwamandan HisbahKwamandan Hukumar...
14/06/2026

”‘Ya’yan Talakawa Ne S**a Fi Yawa a Wuraren da Ake Aikata Bidala da Barna a Katsina” — Kwamandan Hisbah

Kwamandan Hukumar Hisbah ta Jihar Katsina, Dr. Aminu Usman (Abu Ammar), ya bayyana cewa mafi yawan matasan da ake samu a wuraren da ake aikata bidala da sauran ayyukan barna a jihar sun fito ne daga iyalan talakawa.

Dr. Aminu Usman ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da Mobile Media Crew, inda ya ce bincike da gogewar da hukumar ke da ita a ayyukanta na yau da kullum sun nuna cewa matsalolin tattalin arziki, rashin kulawa da tarbiyya na daga cikin abubuwan da ke jefa wasu matasa cikin miyagun ɗabi’u.

Ya jaddada buƙatar haɗin gwiwar iyaye, malamai, shugabannin al’umma da hukumomi wajen ƙarfafa tarbiyyar yara da samar wa matasa hanyoyin dogaro da kai domin rage yawaitar irin waɗannan matsaloli.

Kwamandan ya kuma yi kira ga al’umma da su ci gaba da ba Hisbah haɗin kai wajen yaƙi da munanan ɗabi’u da ayyukan da s**a saɓa wa tarbiyya da dokokin jihar.

IMF Ta Shawarci Nijeriya Ta Ƙaƙaba Sabbin Haraji Kan Fetur da SadarwaAsusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) ya ba gwamnatin...
14/06/2026

IMF Ta Shawarci Nijeriya Ta Ƙaƙaba Sabbin Haraji Kan Fetur da Sadarwa

Asusun Ba da Lamuni na Duniya (IMF) ya ba gwamnatin tarayyar Nijeriya shawarar ƙaƙaba haraji kan kayayyakin man fetur da kuma ayyukan sadarwa domin ƙara yawan kuɗaɗen shiga na gwamnati.

Shawarar na ƙunshe ne a cikin rahoton nazarin tattalin arzikin Nijeriya na shekarar 2026, inda IMF ta bayyana cewa faɗaɗa haraji zuwa wasu muhimman sassa na tattalin arziki zai taimaka wajen samar da kuɗaɗen da ake buƙata domin aiwatar da ayyukan raya ƙasa da shirye-shiryen tallafa wa al’umma.

Asusun ya yi nuni da cewa ƙarin kuɗaɗen shiga daga haraji na iya taimakawa gwamnati wajen rage gibin kasafi, inganta ayyukan more rayuwa da kuma ƙarfafa tattalin arzikin ƙasar.

Sai dai masana da masu ruwa da tsaki na ci gaba da bayyana ra’ayoyi mabambanta kan irin tasirin da ƙarin haraji kan fetur da sadarwa zai iya yi ga ’yan ƙasa da kasuwanci, musamman a daidai lokacin da ake fama da tsadar rayuwa.

Har Yanzu Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Na Hannun Masu Garkuwa da MutaneYayin da Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbata...
14/06/2026

Har Yanzu Matar Marigayi Janar Rabe Abubakar Na Hannun Masu Garkuwa da Mutane

Yayin da Gwamnatin Jihar Katsina ta tabbatar da rasuwar tsohon kakakin rundunar sojojin Najeriya, Manjo Janar Rabe Abubakar (Rtd.), a hannun masu garkuwa da mutane, har yanzu rahotanni na nuna cewa matarsa na ci gaba da kasancewa a hannun waɗanda s**a yi garkuwa da su.

Lamarin ya jawo damuwa da alhini a tsakanin al’umma, musamman ganin cewa marigayin ya rasu ne yayin da ake ci gaba da ƙoƙarin kuɓutar da shi.

Babbar tambayar da mutane da dama ke yi ita ce: Yaya halin da matar marigayin ke ciki a yanzu, kuma yaushe za a samu nasarar kuɓutar da ita?

Ana ci gaba da fatan hukumomin tsaro za su ƙara kaimi wajen ganin an ceto ta cikin koshin lafiya tare da mayar da ita ga iyalanta.

Muna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki Ya kuɓutar da ita cikin aminci, Ya sauƙaƙa mata wannan jarabawa, Ya kuma ba iyalanta haƙurin jure wannan mawuyacin hali.

Allah Ya kuɓutar da ita lafiya, Amin.

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Voice of katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share