17/08/2026
IPAC: Sakamakon Zaben Osun Ya Tabbatar da Aniyar Al’umma Ta Ci Gaba Da Rike Adeleke
Osogbo — Kungiyar Inter-Party Advisory Council (IPAC) reshen Jihar Osun ta taya Gwamnan jihar, Sanata Ademola Adeleke, murnar sake lashe zaben gwamnan jihar, tana mai cewa sakamakon zaben ya nuna aniyar al’ummar jihar na ci gaba da rike shi a matsayin gwamna na tsawon shekaru hudu masu zuwa.
A cikin wata sanarwa da Shugaban IPAC na jihar, Tosin Odeyemi, ya sanya wa hannu, kungiyar ta yaba wa al’ummar Osun bisa yadda s**a fito kwansu da kwarkwata domin kada kuri’unsu cikin lumana.
IPAC ta kuma yabawa INEC, jami’an tsaro, kafafen yada labarai, kungiyoyin farar hula da sauran masu ruwa da tsaki bisa gudunmawar da s**a bayar wajen ganin an gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali.
Kungiyar ta ce sakamakon zaben ya nuna amincewar al’ummar jihar da ayyukan da Adeleke ya gudanar a zangon farko, tare da sabunta musu kwarin gwiwa na ci gaba da jagorancinsa.
IPAC ta bukaci gwamnan da ya tafiyar da mulkinsa na biyu ba tare da nuna banbancin jam’iyya ba, tare da bai wa ‘yan adawa, kwararru, mata, matasa, masu nakasa da hukumomin gargajiya damar bayar da gudunmawarsu wajen ci gaban jihar.
Haka kuma, kungiyar ta bukaci gwamnatin Adeleke da ta tabbatar da cewa rabon mukamai da ayyukan raya kasa ya shafi dukkanin yankunan Sanatoci uku da kananan hukumomi 30 na jihar, ciki har da Area Office.
Ta ce babu wata al’umma da ya kamata ta ji an bar ta a baya, domin samar da hadin kai da ci gaba mai dorewa.
IPAC ta kuma yi kira ga gwamnan da kada sake lashe zabe ya sa a rage kaimi wajen gudanar da ayyukan gwamnati, tana mai cewa wannan zangon na biyu dama ce ta kammala ayyukan da aka fara tare da kirkirar sababbin ayyukan da za su amfani al’umma na dogon lokaci.
Kungiyar ta ce al’ummar Osun na sa ran samun karin ingantaccen aiki a bangarorin ilimi, lafiya, noma, samar da ababen more rayuwa, samar da ayyukan yi ga matasa da walwalar jama’a.
IPAC ta bayyana shirinta na ci gaba da taka rawa a matsayin abokiyar adawa mai gina kasa, inda ta ce za ta rika s**ar manufofin gwamnati ne bisa batun da ya shafi al’umma, tare da mara wa duk wata manufa da ta dace da muradun mutanen Osun baya.
Daga: Voice of Katsina