Da'awatussunnah

Da'awatussunnah Musulunci shine addinin mu 💯
Izzalah Itace aQidarmu
Sunnah Itace Ginshikin Mu
Qur'ani Da Hadith sune Hujjarmu.❤️❤️

*Ya Ubangiji Kai Mai Afuwa Ne,Mai Karamci Ne,Kana Son Afuwa,Ina Roqonka Ka Yimin Afuwa.🤲🏽*  _An kar6o daga Bahaz bn Haki...
11/06/2026

*Ya Ubangiji Kai Mai Afuwa Ne,Mai Karamci Ne,Kana Son Afuwa,Ina Roqonka Ka Yimin Afuwa.🤲🏽*

_An kar6o daga Bahaz bn Hakim, ya ji daga Mahaifinsa shi ma daga Nasa Mahaifin yace : Na ji Manzon Allah S.A.W yana cewa : Tsananin azaba ya tabbata ga wanda yake qirqirar zance domin ya bawa mutane dariya, tsananin azaba ya tabbata a gareshi, tsananin azaba ya tabbata a gareshi.

*_HADISAI 100 MASU FALALA_*Darasi na Bakwai*61. Daga Abdullahi dan Amru Dan As Allah ya yarda dashi ya ce: wani mutum ya...
10/06/2026

*_HADISAI 100 MASU FALALA_*

Darasi na Bakwai

*61. Daga Abdullahi dan Amru Dan As Allah ya yarda dashi ya ce: wani mutum ya tambayi Manzon Allah ﷺ, a cikin Musulunchi mai yafi falala? Sai ya ce: "Kaciyar da abinchi Sannan kayi sallama ga wanda ka sani da wanda baka sani ba".*
متفق عليه

*62. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Bazaku shiga Aljannah ba sai kunyi Imani, bazakuyi Imani ba sai kun so juna, bazan nuna maku wani abu ba wanda idan kuka aikatashi zaku so juna? Ku yaɗa sallama a tsakaninku".*
أخرجه مسلم

*63. Daga Abdullahi Bin Salam Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Ya ku mutane ku yaɗa sallama, ku ciyar da abinchi, ku sadar da zumunta, kuyi salla mutane suna barci, zaku shiga shiga Aljannah da Aminchi".*
حديث حسن صحيح أخرجه الترمذى

*64. Daga Barra'u Dan Azib Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya kasance yana Umurtarmu da abubuwa bakwai: (1) Gaida mara lafiya, (2) Raka Jana'iza, (3) Gaida mai atishawa, (4) Taimakon Mai rauni, (5) Taimakon Wanda aka zalunta, (6) Yaɗa sallama, (7) Barrantar da wanda yai rantsuwa".*
متفق عليه

*65. Daga Imran Dan Hussain Allah ya yarda dashi ya ce: wani mutum ya zo wajen Manzon Allah ﷺ sai ya ce: "ASSALAMU ALAIKUM". sai Manzon Allah ﷺ ya amsa masa sannan ya zauna sai ya ce: "Goma" (Lada goma). Sannan sai ga wani yazo ya ce: "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI". Manzon Allah ﷺ ya amsa masa sannan ya zauna sai ya ce: "Ashirin" (Lada Ashirin). Sai ga wani ya zo ya ce: "ASSALAMU ALAIKUM WARAHMATULLAHI WABARAKATUH". Sai Manzon Allah ﷺ ya amsa masa sannan ya zauna sai ya ce: "Talatin" (Lada talatin).*
حديث حسن أخرجه أبو داود والترمذي

*66. Daga Abi Umamata Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Lallai mafi kusanci ga Allah a cikin mutane shi ne wanda ke fara yi masu sallama".*
أخرجه أبو داود بإسناد جيد،

A wata ruyawar
*67. Daga Abi Umamata Allah ya yarda dashi ya ce: "Ance ya Ma'aikin Allah idan mutum biyu s**a haɗu wazai fara yima wani sallama? Sai ya ce: "Wanda

🌤️🤲 ADDU’AR MU A YAU — YA ALLAH, KA BA MU ABIN DA ZAI SA MU MANTA DA DAMUWAR MU.Alhamdulillahi Rabbil ‘Alameen...Yabo da...
10/06/2026

🌤️🤲 ADDU’AR MU A YAU — YA ALLAH, KA BA MU ABIN DA ZAI SA MU MANTA DA DAMUWAR MU.

Alhamdulillahi Rabbil ‘Alameen...
Yabo da godiya sun tabbata ga Allah.
Mai ba da ni'ima ba tare da an biya Shi ba.
Mai rufa asiri duk da yawan kura-kuranmu.
Mai tausayi ga bayinsa fiye da yadda suke tausayi ga kansu.

Tsira da amincin Allah su tabbata ga
shugabanmu Annabi Muhammad ﷺ,
Iyalansa, sahabbansa da waɗanda s**a bi
Tafarkinsa har zuwa ranar sak**ako.

🤲 Ya Allah...
A yau ba mu zo gare Ka da ƙarfinmu ba.
Ba mu zo da yawan ayyukanmu ba.
Ba mu zo da cancantarmu ba.
Mun zo ne da rauninmu.
Mun zo ne da buƙatarmu.
Mun zo ne da fatan cewa rahamarka ta fi zunubanmu girma

🤲 Ya Allah...
Akwai lokutan da muke nuna wa mutane muna da ƙarfi...
Alhali a zuciyarmu muna yaƙi da damuwa.

Akwai lokutan da muke murmushi...
Alhali muna ɗauke da nauyin da babu wanda ya sani.

Akwai lokutan da muke cewa "lafiya lau"...
Alhali zuciyarmu tana neman taimako.

Ya Rabb...
Kai Ka san abin da muke ɓoyewa.
Kai Ka san abin da ya gaza bakinmu furtawa.

🤲 Ya Allah...
Kada Ka bar mu a inda ƙarfinmu ya ƙare.
Idan hanyoyi s**a rufe, Ka buɗe mana ta falalarka.
Idan tunaninmu ya rikice, Ka ba mu natsuwa.
Idan zuciyarmu ta gaji, Ka ba mu sabuwar ƙwarin gwiwa.
Idan muka kasa ɗaukar nauyin rayuwa,
Ma ɗauke mana abin da ya yi mana nauyi.

🤲 Ya Allah...
Akwai wanda yake jiran labari mai daɗi.
Akwai wanda yake jiran mafita.
Akwai wanda yake jiran waraka.
Akwai wanda yake jiran aikin yi.
Akwai wanda yake jiran aure.
Akwai wanda yake jiran samun zuri'a.

Ya Rabb...
Kafin ƙarshen wannan shekara,
Ka nuna mana ikonKa a cikin buƙatunmu.
Ka mayar da jiranmu ya zama godiya.
Ka mayar da damuwarmu ta zama farin ciki.

🤲 Ya Allah...
Ka sa mu daina dogaro da abin da yake hannun mutane.
Ka haɗa zukatanmu da Kai kaɗai.
Domin wanda ya dogara da Kai ba ya taɓa lalacewa.
Wanda ya nemi taimako daga gare Ka ba ya taɓa komawa da hannu wofi.

🤲 Ya Allah...
Kada Ka gwada mu da abin da zai karya mana imani.
Kada Ka gwada mu da abi

*_HADISAI 100 MASU FALALA_*Darasi na biyar*41. Daga Aisha Allah ya yarda da ita ta ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Raka'o'i b...
09/06/2026

*_HADISAI 100 MASU FALALA_*

Darasi na biyar

*41. Daga Aisha Allah ya yarda da ita ta ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Raka'o'i biyu na alfijir sunfi duniya da abinda ke cikin ta alkhairi".*
رواه مسلم

*42. Daga Ummu Habiba Allah ya yarda da ita ta ce: naji Manzon Allah ﷺ yana cewa: "Babu wani bawa musulmi dazai ma Allah salla a cikin kowane yini raka'a goma sha biyu, na nafila, bana farillah ba, fa ce Allah ya gina masa gida a Aljannah, ko kuma fa ce an gina masa gida a Aljannah".*
رواه مسلم

*Raka'a huɗu kafin azahar da raka'a biyu bayanta, da raka'a biyu bayan Mangariba, da raka'a biyu bayan Isha'i da raka'a biyu kafin Asubahi".*

*43. Daga Ummu Habiba Allah ya yarda da ita ta ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Wanda ya kiyaye yana yin raka'a hudu kafin Azhar da hudu bayan Azhar, Allah zai haramta masa shiga wuta".*
رواه أبو داود والترمذي

*(In kai raka'a biyu zakai sallama, sannan ka ƙara biyu kai sallama)*
Wallahu a'alam

*44. Daga Abdullahi Bin Sa'ib Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ yakasance yana Salla raka'a huɗu bayan rana ta karkata kafin azahar. Sannan ya ce: "Wannan wani lokaci ne da ake buɗe ƙofofin sama, Ni kuma inaso a ɗaga aikina na kwarai a ciki".*
رواه الترمذي وقال حديث حسن

*(Raka'a huɗu zakai gaba ɗaya babu sallama a tsakani. In kai raka'a biyu zaka miƙe ba zakai zaman tahiya ba sai a ƙarshe kai sallama).*
Wallahu a'alam

*45. Daga Abdullahi dan Umar Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Allah yayi jinƙai ga mutumin da yayi raka'a huɗu kafin la'asar".*
حديث حسن رواه أبو داود والترمذي

*46. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Kowace gaɓa ta jikin mutane akwai wajibin sadaka akan ta, Kowace rana da ta fito wannan sadakar na nan (Idan kayi yau gobe dole sai ka sake), ka dai-daita tsakanin mutum biyu sadaka ne, ka taimak**a mutum akan dabbar sa, ka ɗorashi akanta sadaka ne, ko ka ɗora masa kayan shi akan ta sadaka ne, kalma mai daɗi sadakace, kowane taku (tafiya) da kake zuwa masallaci sadaka ne, kawar da ƙaz

DAGA LONDON ZUWA NIGERIA: SAƘON ZUMUNCI MAI GIRMA.Malamanmu kenan daga London sun kammala da’awa, suna shirin dawowa ƙas...
08/06/2026

DAGA LONDON ZUWA NIGERIA: SAƘON ZUMUNCI MAI GIRMA.

Malamanmu kenan daga London sun kammala da’awa,
suna shirin dawowa ƙasar Nigeria.

Wanda abu Islam yake cewa a tare dashi
Da Sheikh Ahmad Tijjani Yusuf Guruntum Hafizahillah
Da Dr Mansur Isah Yelwa Hafizahillah.

Yake cewa:
Bismillah Alhamdulillah,
gani nan ga shehunnaina.
Alhamdulillah anyi taro nan UK lafiya,
an je UK London, an je Birmingham.
Gashi Allah ya nuna mana ƙarshe kowa zai k**a hanyar shi.
Su zasu koma Nigeria, ni kuma zan koma back to Belgium,
Alhamdulillah.

Sheikh Guruntum Hafizahillah yace:
Allah ya saka da alkhairi,
Allah kuma ya sa karɓabbene a wajen Allah,
Allah ya karɓa mana, Allah ya bar zumunci,
Allah ya ƙara maka rayuwa da zurriyarka albarka,
Allah ya ƙara taimakonka wajen ɗauke-ɗauken nan.

Dr Mansur Isah Yelwa Hafizahillah kuma yace:
Abu Islam, abin da zan ce shi ne
wannan ‘yan uwantaka ta addini da akanta muka haɗu.
Ina tuna tun farkon haduwarmu,
mun zo muka same ku a Switzerland,
Kuma gashi yanzu har mun zama ‘yan uwa family ɗaya.
Iyaye ɗaya, zuciya ɗaya.

Muna fata wannan ‘yan uwantaka ta cigaba.
Duk wanda ba irin wannan abota ya yi ta hanyar Allah ba,
idan aka je ranar kiyama abotar ta wargaje.
Amma idan aka yi ta saboda Allah,
kuma akan hanya mai kyau, to za a ji daɗi a duniya.
Kuma mafi girma, idan aka haɗu a lahira,
Mu haɗu a Aljannah in sha Allah.

Abu Islam ya ce:
Ina kaunarku, ku kawo mana ziyara,
Mun kawo malam Guruntum ziyara

Sai dariya ta tashi 🤍
Abu Islam yace ga Bakin gemu,
Darin gemu, da tsaka-tsakiya…

Dr Mansur ya amsa da dariya:
Ni ma bakin gemu ne gaba ɗaya 😄

Sheikh Guruntum ya rufe da addu’a:
Allah ya saukemu lafiya,
Allah ya saka da alkhairi,
Allah ya saka da alkhairi.

Dr Mansur Isah Yelwa kuma ya ce:
Muna godiya ga dukkan waɗanda muka samesu a nan,
da mutanen London, da dukkan ‘yan uwa.
Babu abin da zamu ce sai Allah ya saka muku da alkhairi.

🤍 Wannan shi ne haɗuwar zukata saboda Allah
Ba siyasa ba, ba duniya ba, sai soyayyar addi

ADDU'ARKA GA ƊAN-UWANKA"Addu'arka ga ɗan-uwanka tana da matuƙar ta'asirin gaske akanka da kuma ɗan-uwan naka, domin mala...
08/06/2026

ADDU'ARKA GA ƊAN-UWANKA

"Addu'arka ga ɗan-uwanka tana da matuƙar ta'asirin gaske akanka da kuma ɗan-uwan naka, domin mala'iku zasu amsa addu'arka ga ɗan-uwanka, sannan kuma kaima suyi maka addu'ar irin wacce kayiwa ɗan-uwan naka"

"Basai an tsaya dogon tunani ba, kai da kanka kasan cewa addu'ar mala'iku tafi taka ƙarfi, kaga kenan idan kayiwa ɗan-uwanka addu'ar ashe kaima kanka kayiwa"

"An karɓo daga abu dar'da'i, Allah ya ƙara masa yarda cewa: yaji Manzon Allah ﷺ, yana cewa: idan mutum yayi wa ɗan-uwansa addu'a a bayan idonsa, (a halin ɗan-uwan nasa baya nan), to shima mala'iku zasu (amsa masa) s**e: AMIN, kaima kwatankwacin hakan"
Sunan Abu Dawud (1534)

*_HADISAI 100 MASU TSORATARWA_*Darasi na biyar*41. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "D...
07/06/2026

*_HADISAI 100 MASU TSORATARWA_*

Darasi na biyar

*41. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Duk wanda ya kasance akwai zalunchin (Haƙƙin) ɗan uwansa a hannunshi na mutuncinshi da dukiyarsa, to ya warwareshi kafin ranar da za'a ƙarɓeshi lokacin ba dinari ko dirhami, idan ya yakasance yana da aiki mai kyau, sai a ɗauka a ciki gwargwadon zalunchin da yayi, idan kuma bai dashi, sai a dauki zunuban wanda ya zalunta sai a ɗora masa".*
صحيح أخرجه ابن حبان

*42. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Tabbas zaku mayar da haƙƙoƙi ga masu shi, har ga akuya Mai ƙaho ga mara ƙaho".*
أخرجه البخاري في الأدب المفرد والترمذي

*43. Daga Abi Huraira Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Allah madaukaki ya ce: Mutane uku ni zanyi husuma dasu ranar Al-Qiyama: Mutumin da aka bashi don ni sannan yayi yaudara, da mutumin da ya sai da ɗa sannan yaci kuɗin, da mutumin da ya ɗauki mai aiki (ɗan ƙwadago) mai aikin ya cika aikinsa amma sai ya hanashi ladarsa (Haƙƙinsa)".*
أخرجه البخاري

*44. Daga Abdullahi dan Umar Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Jinkirin biyan bashi ga mawadaci (wanda ke da halin biya) zalunchi ne".*
أخرجه البخاري

*45. Mu'az Dan Jabal Allah dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: dani lokacin da ya aikani Yamen: "......Kaji tsoran Addu'ar wanda aka zalunta domin bata da shamaki tsakaninta da Ubangiji (Allah)".*
متفق عليه

*46. Daga Jabir Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Kuji tsoran zalunchi, domin zalunchi duhu ne ranar Al-Qiyama, Kuma kuji tsoran rowa, domin rowa ita ta halakar da waɗanda s**a zo kafin ku, ta ɗebe su s**a rika zubar da jinanansu, kuma s**a halasta abinda aka haramta musu".*
أخرجه مسلم

*47. Daga Abi umamata Allah ya yarda dashi ya ce: Manzon Allah ﷺ ya ce: "Duk wanda ya yanki wani haƙƙi na wani musulmi da rantsuwarsa, haƙiƙa Allah ya wajabta masa wuta🔥, kuma ya haramta masa Aljannah".*
أخرجه مسلم

*48. Daga Aisha Allah ya yarda da ita ta ce: Manzon Alla

Ya kai wanda matsaloli s**a yi ma dabaibayi, matso kusa ka jiAlbishirinka!Manzon Allah (SAW) yace: "Ubangijinmu Madaukak...
07/06/2026

Ya kai wanda matsaloli s**a yi ma dabaibayi, matso kusa ka ji

Albishirinka!

Manzon Allah (SAW) yace: "Ubangijinmu Madaukaki yana saukowa zuwa saman duniya a kowane dare, idan ya rage d'aya bisa ukun dare na k'arshe, Yana cewa: "Wa zai kira Ni in amsa masa? Wa zai rok'e Ni in ba shi? Wa zai nemi gafara Na in gafarta masa?." Bukhary da Muslim

KANA SON SAMUN LADA DUBU:?"Idan kana so ka sami lada dubu, kuma sannan a kankare maka zunubanka dubu, to ka yawaita yin ...
06/06/2026

KANA SON SAMUN LADA DUBU:?

"Idan kana so ka sami lada dubu, kuma sannan a kankare maka zunubanka dubu, to ka yawaita yin tasbihi, wato faɗin (subhanallah,) sau ɗari za a rubuta maka kyawawan lada dubu, sannan kuma a kankare maka zunubai dubu dominta"

"Ka faɗeta kana mai ƙudurce ma'anarta acikin zuciyarka, sa'annan kuma ka tsarkake zuciyarka a lokacin faɗin nata, duk faɗin Subhanallahi sau ɗari, lallai inshaa Allahu zaka sami kyakkyawan lada guda dubu, da kuma karkaɗe zunubai dubu"

"Manzon Allah ﷺ, yace: shin yanzu ɗayanku zai gajiya wajen samun kyawawan lada guda dubu, sai wani mai tambaya yace: to yanzu ta yaya ɗayan mu zai sami kyawawan lada dubu?, sai (annabi ﷺ,) yace: idan ɗayanku yayi tasbihi (subhanallah) guda ɗari, za'a rubuta masa lada guda dubu, kuma za'a kankare masa zunubai guda dubu"
Jami'i At-tirmiziy (3463)

Address

Kano

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Da'awatussunnah posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share