19/08/2025
Kungiyar GEPIn Ta Yabi Ministan Kuɗi, Wale Edun, Bisa Ƙarfafa Daidaiton Kuɗin Ƙasar Najeriya
Kungiyar Global Economic Policy Initiative (GEPIn) ta yaba wa Mai Girma Ministan Harkokin Kuɗi da Daidaita Tattalin Arzikin Ƙasa, Mista Wale Edun, bisa ci gaban da aka samu wajen daidaita tattalin arzikin Najeriya a ƙarƙashin jagorancinsa.
Da yake jawabi a madadin ƙungiyar, jagoranta, Mista Bernard Okri, ya bayyana cewa biyan bashin fiye da naira tiriliyan 2 na kuɗaɗen kasafin kuɗin manyan ayyuka da s**a rage daga shekarar 2024 na nuna jajircewar Gwamnatin Tarayya wajen dawo da sahihancin kuɗi, ƙarfafa amincewar masu zuba jari, da tabbatar da ci gaba da aiwatar da muhimman ayyukan raya ƙasa a fadin ƙasar.
A cewar GEPIn, wannan matakin ya riga ya fara haifar da sakamako mai kyau.
“Ta hanyar biyan waɗannan bashin, Gwamnatin Tarayya ta rage wa ‘yan kwangila da masu ba da kuɗin ayyuka nauyin da ke kansu, wanda hakan ke ƙarfafa sabon kuzari a ayyukan gina muhimman abubuwan more rayuwa, faɗaɗa damar samar da ayyukan yi, da kuma tallafawa shirin bunƙasar tattalin arzikin gwamnatin nan.”
Kungiyar ta kuma yaba da ƙarin ingancin kuɗin jihohi, inda ta ce ragowar kuɗin jihohi ya ƙaru daga naira tiriliyan 2.8 a shekarar 2023 zuwa naira tiriliyan 7.1. Wannan, a cewar GEPIn, zai ba jihohi damar amfani da ƙarin kuɗaɗen wajen zuba jari a sassa muhimmai kamar gine-gine, kiwon lafiya, da ilimi – waɗanda kai tsaye ke inganta rayuwar ‘yan Najeriya.
“Waɗannan gyare-gyaren na nuna tsari mai ƙa’ida wajen tafiyar da kuɗin gwamnati da kuma bin manufofi da ke ɗan-dan daidaita tattalin arzikin ƙasa,” in ji Mista Okri. “Mun yi imani cewa idan aka ci gaba da wannan tafiya, ba wai kawai zai hanzarta murmurewar tattalin arziki ba ne, har ma zai samar da ginshiƙin da ya fi ƙarfi don bunƙasar da ta shafi kowa da kowa a fadin ƙasa.”
GEPIn ta ƙara kira ga masu ruwa da tsaki da su ba da goyon baya ga ci gaba da gyare-gyaren gwamnatin tarayya, tana mai jaddada cewa haɗin kai ya zama wajibi domin a maida ribar tattalin arziki ta yi tasiri kai tsaye ga rayuwar jama’a.