12/06/2026
BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
BARCIN BAYAN SALLAR ASUBAH
Komawa barci bayan sallar asubah, yana da mutuqar ha'dari ga masu yinsa. Musamman ma wadanda s**a ta'ba fama da matsalar nan ta shafar aljanu (massul jinni) ko sihiri.
Shidai wannan lokacin, wani lokaci ne na musamman wanda Manzon Allah (S.A.W) har addu'a ya yiwa al'ummarsa yana cewa "YA ALLAH KA SANYAWA AL'UMMATA ALBARKA ACIKIN SAMMAKONTA". (Wato Allah ya sanya albarka cikin duk wasu harkokin neman arziki, ko addu'a ko ibadah wacce mutum ya gabatar a irin wannan lokacin).
Watakil sanin wannan ne ya sanya shaidanu suke mutukar zage damtsensu wajen kokarin chutar da duk wanda ya gafala ya koma barci awannan lokaci. Shi yasa zaka ga mafiya yawan masu komawa barci awannan lokacin, s**an sha fama da miyagun mafarkai, dannau, yawan barcin, da sauransu.
Magabata na kwarai, da Sahabbai irin su Abdullahi bn Umar sun kasance suna hana 'ya'yansu da bayinsu komawa barci awannan lokacin. Harma s**an tsawatar sosai idan s**a ga mutum ya kwanta.
Sukan zauna acikin masallacinsu su rika zikirin Allah har sai rana ta fito, sannan su sallaci nafilah raka'a biyu, suyi addu'a sannan su koma gida. Idan ma mutum barcin yake so yayi, suna yin umurnin cewa gara mutum ya bari har sai bayan fitowar rana tukunna.
Kuma idan kasan kana da matsalar shafar Aljanu, duk yadda zuciyarka da jikinka suke son komawa barcin nan kar ka koma!!. Yi kokari ka ribaci irin wadannan lokitan wajen yawaita karatun Alqur'ani da azkar na safe, da sauran azkarai da lazimai, ka shagaltar da zuciyarka wajen tunanin Ubangiji.
Zaka ga kullum sauki yana Qara samuwa, lafiyar jikinka tana Qaruwa, kuma kana Qara samun kusanci da Mahaliccinka.
Allah yasa mudace duniya da lahira Bijahi Rasulillah (S.A.W).