HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll, Emir of gombe

HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll,  Emir of gombe Official page of HRH ALH (Dr ) ABUBAKAR SHEHU ABUBAKAR III, CFR [AMIRUL ZAMAN GOMBE].THE LEGEND IN THE MAKING.
(2)

Official Page to Promote The Eminence Of HRH ALH ABUBAKAR SHEHU ABUBAKAR III

Masallacin Al-Ghamama, Madinar Manz0n Allah (S.A.W)Ɗaya daga cikin wuraren tarih! masu girman daraja a Madina. Wannan sh...
14/08/2026

Masallacin Al-Ghamama, Madinar Manz0n Allah (S.A.W)

Ɗaya daga cikin wuraren tarih! masu girman daraja a Madina.

Wannan shi ne Masallacin Al-Ghamama, wurin da aka ruwaito cewa Manzon Allah ﷺ ya yi Sallar Idi, kuma ya yi addu'ar neman ruwan sama, Allah Ya saukar da gajimare ya ba mutane rahama.

Yayin da na tsaya a wannan wuri, zuciyata ta tuna cewa tarihin Musulunc! ba labari ba ne kawai—gaskiya ce da ta faru a irin waɗannan wurare.

Wata rana watakila kai ma Allah zai ba ka ikon tsayawa a nan, ka ɗaga hannuwanka cikin tawali'u, kana roƙonSa alheri. Kada ka daina addu'a, domin Allah Mai amsa addu'a ne.

Ya Allah, kamar yadda Ka ba ni damar ganin wannan wuri mai albarka, Ka ba duk wanda yake karanta wannan rubutu damar ziyartar Madina da Makkah cikin lafiya da imani.

Ka karɓi ibadunmu, Ka yafe mana zunubanmu, Ka haɗa mu da ManzonKa ﷺ a Aljannar Firdausi.

14/08/2026
Mai Martaba Sarkin Gombe Alh. (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar lll CFR Ya Iso Masallaci Domin Gabatar Da Sallan Jumma'a. Al...
14/08/2026

Mai Martaba Sarkin Gombe Alh. (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar lll CFR Ya Iso Masallaci Domin Gabatar Da Sallan Jumma'a.

Allah Yaja Zamanin Sarki.

MAƁUƁƁUGAR RUWAN SAYYIDA FATIMAH ZAHRA A MADINAShin kun taɓa jin labarin wata maɓuɓɓugar ruwa da ake danganta ta da Sayy...
13/08/2026

MAƁUƁƁUGAR RUWAN SAYYIDA FATIMAH ZAHRA A MADINA

Shin kun taɓa jin labarin wata maɓuɓɓugar ruwa da ake danganta ta da Sayyida Fāṭimah al-Zahrā رضي الله عنها a Madinatul Munawwarah?

A cikin wasu rubuce-rubucen tarihi da s**a shafi Madina, an ambaci wata maɓuɓɓugar ruwa da ake kira “ʿAyn Fāṭimah” (عين فاطمة) — wato Maɓuɓɓugar Fāṭimah.

Ana danganta wannan maɓuɓɓugar da wurin da ake amfani da ruwanta wajen ban-ruwa da shayar da gonaki, domin amfanin mazauna yankin.

Wannan labari yana ƙara nuna mana irin yadda ruwa, gonaki da sadaka s**a kasance masu muhimmanci a tarihin Madina.

Tarihin Madina yana ɗauke da abubuwan ban mamaki da dama.

Allah Ya ƙara mana ƙaunar Manzon Allah ﷺ da Ahlul Baiti رضي الله عنهم, Ya kuma azurta mu da ziyartar Madinatul Munawwarah.

JIYA BA YAU BA...A 1920 aka fara aiki kawo wutar lantarki zuwa lardin kano Wanda a wan nan Lokacin kano ta zama gari na ...
13/08/2026

JIYA BA YAU BA...

A 1920 aka fara aiki kawo wutar lantarki zuwa lardin kano Wanda a wan nan Lokacin kano ta zama gari na farko da aka fara aikin kawo wutan lantarki Arewacin Nigeria.

Allah ya jikan magabatan mu.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM KU DUBA WANNAN QAUNA NA ANNABINMU MUHAMMADU (S.A.W)Riwayah daga Sayyiduna Abbas bn Mirdas (ra...
13/08/2026

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

KU DUBA WANNAN QAUNA NA ANNABINMU MUHAMMADU (S.A.W)

Riwayah daga Sayyiduna Abbas bn Mirdas (radhiyal-Lahu anhu) yace :

"Hakika Manzon Allah (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam) a yammacin ranar arfah yayi ma al'ummarsa addu'ar neman gafara. Sai aka amsa masa da cewar :

"HAKIKA NI NA GAFARTA MUSU AMMA BANDA AZZALUMI DOMIN HAKIKA NI SAI NA KARBA MA WANDA AKA ZALUNTA HAKKINSA DAGA WAJENSA".

Sai Manzon Allah (S.A.W) yace : "YA UBANGIJI IDAN KASO ZAKA BAYAR DA ALJANNAH GA WANDA AKA ZALUNTA. SHI KUMA AZZALUMIN KA GAFARTA MASA".

Ba'a amsa masa awannan Yammacin ba. Amma yayin da ya wayi gari a Muzdalifah ya maimaita addu'ar sai aka amsa masa abinda ya roka. Don haka sai yayi dariya ko murmushi (sallal Laahu alaihi wa aalihi wa sallam).

Sai Sayyiduna Abubakrin da Sayyiduna Umar (Radhiyallahu anhuma) kowannensu yace "Mahaifina da Mahaifiyata fansa ne gareka Ya Rasulallahi.. Hakika wannan wani lokaci ne wanda baka saba yin dariya (murmushi) acikinsa ba. Menene ya sanyaka dariya?? Allah shi Qara faranta ranka.

Sai Manzon Allah (S.A.W) yace "HAKIKA IBLEES MAKIYIN ALLAH YAYIN DA YASAN CEWA ALLAH YA AMSHI ROKONA KUMA YA GAFARTA MA AL'UMMATA, SAI YA RIKA 'DIBAN QASA YANA ZUBAWA AKANSA YANA KIRA MA KANSA AZABA DA LALACEWA (WATO YANA EEHU YANA CEWA "YA SHIGA UKU!! YA LALACE!! TUNDA AN GAFARTA MA AL'UMMAR ANNABI MUHAMMADU).

"TO ABINDA NA GANI NA BAKIN CIKINSA DA FIRGICINSA SHINE YA SANYANI DARIYA".

(ABU DAWUD DA IBNU MAAJAH NE S**A RUWAITOSHI).

BAYANI
********
To 'yan uwa kunji halin tsinanne, jefaffe daga rahama.. Wato Shaitan (Iblees) Makiyin Allah kuma Babban Makiyinmu.

Wanda har abada dashi da Zuriyarsa burinsu shine su hallakar damu, su chutar damu, su lalata ayyukanmu, su ga cewa Mafiya yawan 'Ya'yan Adam (as) sun zama abokan zamansu acikin wuta.

Allah Madaukakin Sarki da kansa yace "HAKIKA SHAITAN MAQIYINKU NE. TO KU MA KU RIKESHI AMATSAYIN ABOKIN GABA.. ".

Kuma yace "KADA KUBI SAWUN SHAITAN. HAKIKA SHI MAQIYINKU NE MAI BAYYANAR DA QIYAYYA".

To hakanan kuma bamu da cikakken masoyi irin Annabinmu Shugabanmu Muhammadu (sallal Lahu alaihi wa aalihi wa sallam) wanda ko yaushe nufinsa garemu shine alkhairi. Addu'arsa kullum garemu yake yinta. Ya roka mana gafara da afuwa da rahamar Ubangiji. Kuma yayi ta maimaita rokon har sai Allah ya amsa masa.

Wallahi duk irin Soyayya da Qaunar da zamu yi masa, ba zamu iya kwatanta koda kashi guda cikin kashi dubu na irin Qaunar da yake yi mana ba.

Allah da kansa yana yi masa kirari yana cewa : "SHI (ANNABI MUHAMMADU) MAI MUTUKAR RANGWAME NE DA JIN QAI GA MUMINAI".

Ya Rasulallahi mun gode Mun gode. Allah ya saka maka da mafi girman sakamakon da yake yiwa Annabawa da Manzanni bisa al'ummatansu.

Salatin Allah da amincinsa su tabbata agareka Ya Masoyin Allah bisa gwargwadon adadin abinda ilimin Ubangiji ya tattaro.. tare da iyalan gidanka Tsarkaka da dukkan Sahabbanka da Salihan mabiyanka baki daya.

Ameen YA HAYYU YA QAYYUM.🙏

A cikin tarihin wannan wuri, an ruwaito cewa Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana tsayawa a nan idan ya dawo daga tafiya...
12/08/2026

A cikin tarihin wannan wuri, an ruwaito cewa Manzon Allah (S.A.W) ya kasance yana tsayawa a nan idan ya dawo daga tafiya da dare, ya kwana a wurin, sannan idan gari ya waye sai ya ci gaba da tafiya zuwa Madina.

Haka kuma, an ruwaito cewa Mala’ika Jibrilu عليه السلام ya zo wa Manzon Allah ﷺ da umarni da ya yi sallah a wannan kwari mai albarka.

Wuri ne da yake ɗauke da tarihin Musulunci mai matuƙar muhimmanci.

Duk wanda baizo wannan Birnin na madinar Manzon Allah SAW ba Allah kabashi ikon zuwa acikin sauki Nan kurkusa bada jimawa ba.

JIYA BA YAU BA...Masu karban kudin aikinsu ranar asabar ranace ta biyan kudin sati a arewacin Najeriya, daga ma aikacin ...
12/08/2026

JIYA BA YAU BA...

Masu karban kudin aikinsu ranar asabar ranace ta biyan kudin sati a arewacin Najeriya, daga ma aikacin Kamfanin Pengal Mine, anyi hoton cikin shekarar 1944.

Allah ya jikan magabatan mu.

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll, Emir of gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Shortcuts

Share

Category