HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll, Emir of gombe

HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll,  Emir of gombe Official page of HRH ALH (Dr ) ABUBAKAR SHEHU ABUBAKAR III, CFR [AMIRUL ZAMAN GOMBE].THE LEGEND IN THE MAKING.
(3)

Official Page to Promote The Eminence Of HRH ALH ABUBAKAR SHEHU ABUBAKAR III

12/06/2026
Mai Martaba Sarkin Gombe Alh (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar lll CFR Ya Shirya Tsaf Domin Tafiya Sallan Jumma'a. Allah Ya ...
12/06/2026

Mai Martaba Sarkin Gombe Alh (Dr.) Abubakar Shehu Abubakar lll CFR Ya Shirya Tsaf Domin Tafiya Sallan Jumma'a.

Allah Ya Karawa Sarki Imani Da Daukaka.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM BARCIN BAYAN SALLAR ASUBAHKomawa barci bayan sallar asubah, yana da mutuqar ha'dari ga masu y...
12/06/2026

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

BARCIN BAYAN SALLAR ASUBAH

Komawa barci bayan sallar asubah, yana da mutuqar ha'dari ga masu yinsa. Musamman ma wadanda s**a ta'ba fama da matsalar nan ta shafar aljanu (massul jinni) ko sihiri.

Shidai wannan lokacin, wani lokaci ne na musamman wanda Manzon Allah (S.A.W) har addu'a ya yiwa al'ummarsa yana cewa "YA ALLAH KA SANYAWA AL'UMMATA ALBARKA ACIKIN SAMMAKONTA". (Wato Allah ya sanya albarka cikin duk wasu harkokin neman arziki, ko addu'a ko ibadah wacce mutum ya gabatar a irin wannan lokacin).

Watakil sanin wannan ne ya sanya shaidanu suke mutukar zage damtsensu wajen kokarin chutar da duk wanda ya gafala ya koma barci awannan lokaci. Shi yasa zaka ga mafiya yawan masu komawa barci awannan lokacin, s**an sha fama da miyagun mafarkai, dannau, yawan barcin, da sauransu.

Magabata na kwarai, da Sahabbai irin su Abdullahi bn Umar sun kasance suna hana 'ya'yansu da bayinsu komawa barci awannan lokacin. Harma s**an tsawatar sosai idan s**a ga mutum ya kwanta.

Sukan zauna acikin masallacinsu su rika zikirin Allah har sai rana ta fito, sannan su sallaci nafilah raka'a biyu, suyi addu'a sannan su koma gida. Idan ma mutum barcin yake so yayi, suna yin umurnin cewa gara mutum ya bari har sai bayan fitowar rana tukunna.

Kuma idan kasan kana da matsalar shafar Aljanu, duk yadda zuciyarka da jikinka suke son komawa barcin nan kar ka koma!!. Yi kokari ka ribaci irin wadannan lokitan wajen yawaita karatun Alqur'ani da azkar na safe, da sauran azkarai da lazimai, ka shagaltar da zuciyarka wajen tunanin Ubangiji.

Zaka ga kullum sauki yana Qara samuwa, lafiyar jikinka tana Qaruwa, kuma kana Qara samun kusanci da Mahaliccinka.

Allah yasa mudace duniya da lahira Bijahi Rasulillah (S.A.W).

JIYA BA YAU BA...Wannan Hoton Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto Firimiyan jahar arewa a cikin wani aji a makarantar Plat...
11/06/2026

JIYA BA YAU BA...

Wannan Hoton Sir Ahmadu Bello Sardaunan Sokoto Firimiyan jahar arewa a cikin wani aji a makarantar Plateau Provincial Secondary School, Kuru (wadda a yanzu ake kira Government Science School, Kuru), a shekarar 1962. yau shekara 64 kenan da kai wannan ziyarar.

Allah ya jikan magabatan mu.

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM JAN HANKALI MAI FALALAN GASKE:MASU YIN GULMASubhanallah!! Hakika Gulma ba Qaramar masifa bace...
11/06/2026

BISMILLAHIR RAHMANIR RAHIM

JAN HANKALI MAI FALALAN GASKE:

MASU YIN GULMA

Subhanallah!! Hakika Gulma ba Qaramar masifa bace!! Ba karamin bala'I bane. Masu yinta suna cikin asara marar iyaka.

Annabi (S.A.W) yace: "Ranar da akayi Isra'I dani, na Wuce ta kusa da wasu Mutane suna da farce na azurfa, suna yakushin fuskokinsu dashi. Sai nace: "Wadannan kuma su waye Ya Jibreelu?".

Sai yace "Sune Mutanen da suke Gulmar Jama'a, kuma suna afkawa cikin mutuncinsu".
(Abu Dawud).

Watarana Annabi Eisa (as) sun hadu da Iblees (L.A) sai ya ganshi rike da zuma ahannunsa guda. A daya hannun kuma Baqar Qasa ce.

Da Annabi Eisa (as) ya tambayeshi game da haka sai yace: "Ita wannan Zumar ina sanyata ne akan harshen masu GULMA, shi yasa da zarar sun fara yinta sai an sauraresu. Kuma idan s**a fara sai sun idar. Ita kuma wannan baqar Qasar, ina sanyata ne akan fuskokin marayu. Ina munana kamanninsu shi yasa zaka ga Mutane suna Kyamatarsu, basu iya yi musu alkhairi".

Hatamul Asammu (rah) yace: "Masu gulma da masu annamimanci, sune birrai na 'yan wuta, Makaryata kuma sune karnukan 'Yan wuta. Masu hassada kuma sune aladun 'yan wuta".

Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!!

Ya Allah kayi mana tsari daga sharrin gulma da magulmata da Annamimanci da masu yinsa Bijahi Rasulillahi (S.A.W).🙏🙏🙏

Masjid Annabawi Madinah Al'munawwarah.
10/06/2026

Masjid Annabawi Madinah Al'munawwarah.

Address

Gombe

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when HRH Alh. Abubakar Shehu Abubakar lll, Emir of gombe posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share

Category