12/12/2022
LABARI DA ƊUMI ƊUMI: “Akwai Yiyuwar Za’a Dawo Da Gawar Fir’auna Najeriya.
Wani ɗalibi mai suna Ashrab Al-Hazard dake karatu a jami’ar al’azhar ta ƙasar masar ya ce ya kamata a ɗauko gawar Fir’auna daga ƙasar Masar wato Egypt a dawo da ita Najeriya.
APA Hausa ta rawaito cewa, Yaron yace yana so a dawo da Gawar Fir'auna Nigeria ne Saboda nan ne tafi dacewa a adana ta domin kuwa kusan dukkan ƴan Najeriya kashi 85 basu da gaskiya da kuma tausayin junansu.
Ɗalibin ya bayyana cewar babu inda ake tafka rashin tausayi kamar ƙasar Najeriya kamar yadda ya rubuta a shafinsa na Instagram.
Kunji fa yaya kuke kallon wannan kira na shi, shin Kuna goyon bayan a dawo da gawar Fir'auna kasar Mu Najeriya?
Ku baiyyana ra'ayoyin Ku, sai Muji jahar da ya kamata akai shi🤣