03/02/2026
ME YASA AKE KIRAN IMAM MAHDI(AJF) DA SUNAYEN (AL-QAEEM DA AL-MUNTAZAR)
An ruwaito cewa Abu Jafar Imam Muhammad bin Ali AlRida (AS) ya ce:- "Limami a bayana shine ɗana, Ali AlNaqi (AS), Umarninsa Umarnina ne, kalamansa kalamaina ne, yin biyayya a gareshi yin biyayya a gareni ne.
Imam a bayansa shine ɗansa Hasan AlAskari(AS). Umarninsa umarnin mahaifinsa ne, maganganunsa itace maganar mahaifinsa, kuma biyayya gareshi ita ce biyayya ga mahaifinsa."
Sai Imam ya yi shiru!
Sai mai tambaya ya ce:- "Ya kai ɗan Manzon Allah, wanene Imam bayan Imam Hasan Askari (AS)?"
Imam (AS) ya yi kuka sosai sannan ya ce, "Bayan Imam Hasan Askari (AS) shine ɗansa Al'Qaeem bil Haqq (Wato mai tsayuwa akan Gaskiya), Mai jira."
Sai mai tambaya ya sake tambaya yace:- "Ya kai ɗan Manzon Allah, me yasa ake kiransa AlQa'eem (AS)?"
Imam(AS) ya ce, "Domin zai tashi bayan mutuwar ambatonsa da riddarsa (murtad wato, kin amincewa) na yawancin waɗanda s**a yi imani da Imamancinsa."
Sai mai tambaya yace, "Me yasa ake kiransa da Mai jira (Al-Muntazar)?"
Imam (AS) ya ce, "Domin zai yi ɓuya(Gaiba) na kwanaki da yawa na tsawon lokaci.
Don haka masu gaskiya/aminci za su jira tashinsa, masu shakka kuma za su ƙi Shi, waɗanda s**a ƙi/ƙarya za su yi izgili da ambatonSa (zekr) kuma waɗanda s**a sanya lokaci don sake bayyanawarsa za su yi ƙarya, waɗanda za su yi gaggawa (gaggawa game da sake bayyana) a lokacin Ghaybah za su halaka, waɗanda kuma za su miƙa wuya a lokacin ɓoyewarsa (Ghaybah) za su tsira."
Cikin Littafin Kamal Aldeen na Shaikh Saduq, Babi na 36, Hadith. 3
Allah (swt) Ya gaggauta sake bayyanar wanda da bayyanar wanda da bayyanar sane Duniya zata zama cikin aminci da bayan ya kawar da zalunci.
Happy Birthday Leader Sayyid Ibraheem Zakzaky(H)
©️ Al-Muntazar Group
https://www.facebook.com/AlmuntazarGraphics