BabangidaSalihu

BabangidaSalihu Muna tura muku ingantaccin labaran kasarmu ta najeriya Labaru da dumi dumin su

24/07/2026
ZIYARAR BANGIRMA DA NEMAN GOYON BAYA DOMIN ƘARFAFA NASARAR JAM'IYYAR APC A YANKIN KOKO-BESSE GABANIN ZAƁEN 2027Dan takar...
24/07/2026

ZIYARAR BANGIRMA DA NEMAN GOYON BAYA DOMIN ƘARFAFA NASARAR JAM'IYYAR APC A YANKIN KOKO-BESSE GABANIN ZAƁEN 2027

Dan takarar kujerar Majalisar Dokokin Jihar Kebbi mai wakiltar Koko-Besse a ƙarƙashin Jam'iyyar APC, Hon. Abdurrahman Mamuda Wafa Koko (Giwa), tare da tawagarsa, sun kai ziyarar bangirma da neman shawarwari ga Mai Girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko (Shehu Fari) a Babban Birnin Tarayya, Abuja, ranar Alhamis, 23 ga Yuli, 2026.

wannan ziyara don neman shawarwari tare da neman ci gaba da samun goyon baya da gudummawar Mai Girma Ciroman Koko, wanda ya kasance daya daga cikin manyan jiga-jigan APC da s**a taka muhimmiyar rawa wajen samun nasarorin da Jam'iyyar APC ta samu a yankin Koko-Besse da maiyama a zabukan da s**a gabata.

A yayin tattaunawar, an yi nazari kan muhimman dabarun da za su ƙara ƙarfafa haɗin kai a tsakanin shugabanni, magoya baya da mambobin jam'iyya, domin tabbatar da cewa Jam'iyyar APC ta samu nasara a babban zaɓen shekarar 2027.

Tawagar ta kuma roƙi Mai Girma Ciroman Koko da ya ci gaba da ba da irin gudummawa, shawarwari da goyon bayan da ya saba bai wa Jam'iyyar APC da 'yan takarar Jam'iyyar APC daga matakai daban-daban a yankin Koko-Besse domin samun nasara a zaɓe mai zuwa.

A nasa jawabin, Mai Girma Ciroman Koko, Alhaji Shehu Mohammed Bello Koko (Shehu Fari) ya tabbatar da cewa zai ci gaba da bai wa Jam'iyyar APC da dukkan 'yan takararta goyon baya da gudummawar da za ta taimaka wajen samun gagarumar nasara a zaɓen shekarar 2027.

Ya bayyana cewa wannan matsaya ta samo asali ne daga gamsuwarsa da irin ayyukan alheri, ci gaba da sauye-sauyen da Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu) ke aiwatarwa domin inganta rayuwar al'ummar jihar. Saboda haka, ya bayyana aniyarsa ta yin duk mai yiwuwa domin ganin Gwamnan ya samu damar komawa kan mulki a karo na biyu, tare da tabbatar da nasarar dukkan 'yan takarar Jam'iyyar APC domin su ci gaba da tafiyar da manufofin ci gaba da s**a amfani al'ummar Jihar Kebbi.

Haka kuma, an tattauna muhimmancin bai wa matasa dama a harkokin siyasa, tare da ƙarfafa su su shiga a dama da su wajen jagoranci da ayyukan jam'iyya. An jaddada cewa matasa su ne ginshiƙin nasarar kowace jam'iyya, kuma haɗin kansu, jajircewarsu da kishinsu za su taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da nasarar APC a zaɓen shekarar 2027.

A ƙarshe, tawagar ta yaba da kyakkyawar tarbo, shawarwari masu amfani da kuma jajircewar Mai Girma Ciroman Koko wajen haɗa kan al'umma da ci gaba da tallafa wa Jama'a da APC. Sun bayyana cewa irin wannan haɗin kai da goyon baya zai zama babban ginshiƙi na samun nasarar jam'iyyar da dukkan 'yan takararta a babban zaɓen shekarar 2027.

Haɗin Kai, Goyon Baya da Kyakkyawan Tsari Su Ne Mabuɗin Nasarar APC a Koko-Besse da Jihar Kebbi a 2027.

Ciroman Koko Media Team
24/07/2026

A MADADIN MAI GIRMA SARKIN KOKO, ALHAJI MOHAMMED BELLO KOKO II, DA DAUKACIN AL'UMMAR MASARAUTAR KOKO, ANA MIƘA SAƘON TAY...
22/07/2026

A MADADIN MAI GIRMA SARKIN KOKO, ALHAJI MOHAMMED BELLO KOKO II, DA DAUKACIN AL'UMMAR MASARAUTAR KOKO, ANA MIƘA SAƘON TAYA MURNA GA CP DANBABA MOHAMMED BISA SAMUN MUƘAMIN COMMISSIONER OF POLICE (CP)

Da sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jin Ƙai.

Mai Girma Sarkin Koko, Alhaji Mohammed Bello Koko II, tare da daukacin al'ummar Masarautar Koko, suna miƙa saƙon taya murna ta musamman ga ɗaya daga cikin fitattun 'ya 'yan Al'ummar Masarautar Koko, CP Danbaba Mohammed bisa wannan babban matsayi da Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙaddara masa na zama Commissioner of Police (CP) a Rundunar 'Yan Sandan Najeriya.

Wannan ɗaukaka ba ta tsaya a gare ka kaɗai ba; ɗaukaka ce ga iyalanka, Masarautar Koko, Jihar Kebbi da kuma ƙasa baki ɗaya. Haƙiƙa, wannan ci gaba ya tabbatar da cewa ƙwazo, jajircewa, biyayya ga doka da riƙon amana su ne ginshiƙan samun nasara.

Mai Girma Sarkin Koko yana addu'ar Allah Maɗaukakin Sarki Ya ƙara maka lafiya, hikima, basira da ƙarfin guiwa domin gudanar da wannan babban nauyi cikin adalci, gaskiya da kishin ƙasa. Allah Ya sanya wannan matsayi ya zama sanadin ƙarin ɗaukaka da nasarori a rayuwarka.

A madadin Masarautar Koko baki ɗaya, muna kuma bayyana matuƙar godiya da yabawa gare ka bisa irin gudummawar da kake bayarwa wajen taimakawa matasan Masarautar Koko su samu shiga cikin Rundunar 'Yan Sandan Najeriya. Wannan kyakkyawan aiki da kake yi ya nuna ƙaunarka ga al'ummarka da kuma kishinka na ganin matasa sun samu aikin yi da kyakkyawar makoma.

Jama'a basu mantawa da waɗanda aka share musu hanya zuwa ga ci gaba. Saboda haka, Masarautar Koko tana alfahari da kai, kuma tana yabawa tare da godiya bisa wannan gagarumar gudummawa da kake ci gaba da bayarwa.

Muna roƙon Allah (SWT) Ya ci gaba da tsare ka, da daukaka, Ya ba ka ikon ci gaba da yi wa Najeriya, jahar kebbi da al'umma hidima cikin gaskiya, adalci da riƙon amana.

Muna sake taya ka murna, muna yi maka fatan alheri da ƙarin nasarori a gaba. Allah Ya ƙara ɗaukaka da arziki. Amin.

Allah Ya kiyaye Mai Girma Sarkin Koko, Ya ɗaukaka Masarautar Koko da jahar kebbi Ya kuma ci gaba da baka nasara. Ameen

Masarautar Sarkin Koko
22/07/2026

HAKIMAI, MALAMAI DA LIMAMAN MASARAUTAR KOKO SUN GUDANAR DA ADDU'AR CIKA SHEKARA UKU DA RASUWAR MARIGAYI MAI GIRMA SARKIN...
21/07/2026

HAKIMAI, MALAMAI DA LIMAMAN MASARAUTAR KOKO SUN GUDANAR DA ADDU'AR CIKA SHEKARA UKU DA RASUWAR MARIGAYI MAI GIRMA SARKIN KOKO, MALAM MOHAMMADU BELLO KOKO NA I

A yau, 21 ga Yuli, 2026, ya cika shekaru uku da rasuwar Marigayi Mai Girma Sarkin Koko, Malam Mohammadu Bello Koko Na I, wanda ya rasu a ranar 21 ga Yuli, 2023.

Domin tunawa da wannan rana, Hakimai, Malamai da Limaman Masarautar Koko sun gudanar da addu'o'i na musamman, suna roƙon Allah Maɗaukakin Sarki da Ya gafarta masa kurakuransa, Ya yalwata masa rahama, Ya sanya kabarinsa ya zama lambu daga cikin lambunan Aljanna, Ya haskaka masa kabari, Ya kuma ba shi matsayi mafi girma a Aljannatul Firdausi.

Haka kuma, an yi addu'ar Allah Ya ba iyalansa, Masarautar Koko da al'ummar Musulmi baki ɗaya haƙurin jure rashinsa, Ya kuma ci gaba da ɗaukaka Masarautar Koko cikin zaman lafiya, haɗin kai da ci gaba.

Allah Ya jiƙan Marigayi Mai Girma Sarkin Koko, Malam Mohammadu Bello Koko Na I. Allah Ya gafarta masa, Ya karɓi kyawawan ayyukansa, Ya sanya Aljannatul Firdausi ta zama makomarsa. Allah Ya jiƙan dukkan Musulman da s**a riga mu gidan gaskiya. Amin Ya Rabbal 'Alamin.

Masarautar Mai Girma Sarkin Koko
21/07/2026

AN K**A 'YAN TA'ADDA A KADUNARahoto Daga Shafin Datti AssallafyDazu wajen misalin karfe 12 na rana Sojojin Nigeria sun k...
13/07/2026

AN K**A 'YAN TA'ADDA A KADUNA

Rahoto Daga Shafin Datti Assallafy

Dazu wajen misalin karfe 12 na rana Sojojin Nigeria sun k**a wadanann 'yan ta'adda 'yan kab¡|ar birom a jihar Kaduna

Sun yi safaran bindigogi ne a cikin mota daga Jos jihar Pilato zasu kai zuwa Minna a jihar Niger, sun bi ta Kaduna sai Sojoji s**a k**a su

Gasu nan 'yan ta'adda ne har da mace, kuma babu Musulmi ko guda daya a cikin su

Irin wannan labarin su Rev Ezekiel Dachomo basa so a fada, kuma basa so ya yadu saboda 'yan uwansa ne

Mu a matsayin mu na Musulmai da aka karantar damu adalci, mun san cewa wadannan 'yan ta'adda ba karantarwan addininsu s**a bi ba

Allah Ka tona asirin azzalumai maciya amana

AN ƘADDAMAR DA RABON TAKIN ZAMANI KYAUTA  GA AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR MULKI TA KOKO-BESSEA yau Litinin, 13 ga Yuli, 2026...
13/07/2026

AN ƘADDAMAR DA RABON TAKIN ZAMANI KYAUTA GA AL'UMMAR ƘARAMAR HUKUMAR MULKI TA KOKO-BESSE

A yau Litinin, 13 ga Yuli, 2026, Mai Girma Shugaban Ƙaramar Hukumar Mulki ta Koko-Besse, Hon. Sirajo Usman Koko (Dan Gwaggo), ya jagoranci ƙaddamar da rabon buhunan taki 3,056 da Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), ya ware domin tallafa wa manoman ƙaramar hukumar.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa an tsara rabon takin ne ta runfunan zaɓe domin tabbatar da adalci da gaskiya. Saboda haka, ba a ware takin ga ƙungiyoyi, ma'aikata, sarakuna, shugabanni, 'yan siyasa ko 'yan jarida ba. Kowane mai hakki zai karɓi rabonsa ne a runfar zaɓensa k**ar sauran al'umma.

A jawabinsa, Hon. Sirajo Usman Koko ya tabbatar da cewa gwamnatin ƙaramar hukumar ta aiwatar da umarnin Mai Girma Gwamna ba tare da ƙari ko ragi ba. Ya kuma bayyana cewa an raba dukkan takin da aka kawo zuwa runfunan zaɓe ba tare da cire ko buhu guda ba.

Domin sauƙaƙa aikin rabon, gwamnatin Ƙaramar Hukumar Koko-Besse ta ɗauki nauyin jigilar dukkan takin zuwa mazabu da runfunan zaɓe da kuɗinta, domin kauce wa duk wata matsala ta sufuri ko wani ƙarin kuɗi ga al'umma.

A madadin Mai Girma Kwamishinan Kananan Hukumomi da Masarautu, Hon. Garba Umar Dutsin Mari, wakilinsa Hon. Yahaya Bello Koko (Sarkin Gabas) ya yi bayanin tsarin rabon, inda ya jaddada cewa manufar ita ce tabbatar da cewa tallafin gwamnati ya isa ga waɗanda aka tanada wa cikin gaskiya da adalci.

Taron ya samu halartar wakilan Masarautar Koko-Besse, shugabannin APC, kansiloli, hakimai, jami'an tsaro, wakilan 'yan majalisu da dimbin al'ummar Ƙaramar Hukumar Koko-Besse.

Abin lura shi ne, an raba buhunan taki 3,056 zuwa runfunan zaɓe 191, inda kowace runfa ta samu buhu 16, abin da ya tabbatar da daidaito wajen rabon.

Haka kuma, an bayyana cewa shugaban kwamitin rabon taki na kowace Ward shi ne Kansilan Ward ɗin, yayin da Shugaban APC na Ward yake matsayin Sakataren Kwamitin tare da sauran mambobi. Don haka, duk wata matsala da ta taso a kowace runfa tana ƙarƙashin jagororin wannan runfar.

An kammala taron cikin kwanciyar hankali da nasara.

Allah Ya saka wa Mai Girma Gwamnan Jihar Kebbi, Comrade Dr. Nasir Idris (Kauran Gwandu), da alheri, Ya ƙara masa lafiya da nasara. Haka kuma Allah Ya ƙara wa Hon. Garba Umar Dutsin Mari da Hon. Sirajo Usman Koko (Dan Gwaggo) hikima da ƙarfin ci gaba da yi wa al'umma hidima.

Ciroman Koko Media Team
13/07/2026

28/06/2026

Yara Manyan Gobe

28/06/2026

Let's go
Active Followers

24/06/2026

Let's Go
Morning Engagement

23/06/2026

Innah lillahi wa innah ilaihir raji'un 😭😭😭

Alh. Muhammadu Umar Mai Barga Besse (Former Apc Chairman Koko-Besse), ubangiji Allah yayi maka rahama kuma Allah ya isar muna akan wannan zalumcin, Amin, Allah ya tona asirin Wadan da ke da hannu cikin wannan mummunan zalinci Amin.

Address

Abuja

Telephone

+2348027746672

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when BabangidaSalihu posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The Business

Send a message to BabangidaSalihu:

Shortcuts

Share